< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
A Melody of David. When he was in the Wilderness of Judah. O God, my GOD, thou art, Earnestly do I desire thee, —My soul thirsteth for thee, My flesh fainteth for thee, In a land—dry, and weary for want of water, —
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
In like manner as, in the sanctuary, I have had vision of thee, To behold thy power and thy glory.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Because better is thy lovingkindness than life, My lips, aloud shall praise thee!
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Thus, will I bless thee while I live, In thy Name, will I lift up mine outspread hands:
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
As with fatness and richness, shall my soul be satisfied, And, with joyfully shouting lips, shall my mouth utter praise.
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Should I call thee to mind upon my couch, In the watches of the night, would I breathe soft speech of thee.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
For thou hast become a help unto me, —And, in the shadow of thy wings, will I shout for joy.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
My soul hath run clinging to thee, On me, hath thy right hand laid hold.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
When, they, to crush it, would seek my life, They shall go into the lower parts of the earth:
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Every one shall be given up into the power of the sword, The portion of jackals, shall they become.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
But, the king, shall rejoice in God, —Every one shall glory who sweareth by him, For the mouth of them who speak falsehood, shall be stopped.

< Zabura 63 >