< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
A Psalme of David. When he was in the wildernesse of Judah. O God, thou art my God, earely will I seeke thee: my soule thirsteth for thee: my flesh longeth greatly after thee in a barren and drye land without water.
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Thus I beholde thee as in the Sanctuarie, when I beholde thy power and thy glorie.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
For thy louing kindnesse is better then life: therefore my lippes shall prayse thee.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Thus will I magnifie thee all my life, and lift vp mine hands in thy name.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
My soule shalbe satisfied, as with marowe and fatnesse, and my mouth shall praise thee with ioyfull lippes,
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
When I remember thee on my bedde, and when I thinke vpon thee in the night watches.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Because thou hast bene mine helper, therefore vnder the shadow of thy wings wil I reioyce.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
My soule cleaueth vnto thee: for thy right hand vpholdeth me.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Therefore they that seeke my soule to destroy it, they shall goe into the lowest partes of the earth.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
They shall cast him downe with the edge of the sword, and they shall be a portion for foxes.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
But the King shall reioyce in God, and all that sweare by him shall reioyce in him: for the mouth of them that speake lyes, shall be stopped.

< Zabura 63 >