< Zabura 62 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
Müzik Şefi Yedutun için - Davut'un mezmuru Canım yalnız Tanrı'da huzur bulur, Kurtuluşum O'ndan gelir.
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Tek kayam, kurtuluşum, Kalem O'dur, asla sarsılmam.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
Birini ezmek için daha ne vakte kadar Hep birlikte üstüne saldıracaksınız, Eğri bir duvara, Yerinden oynamış bir çite saldırır gibi?
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
Tek düşünceleri onu doruktan indirmektir. Yalandan zevk alırlar. Ağızlarıyla hayırdua ederken, İçlerinden lanet okurlar. (Sela)
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
Ey canım, yalnız Tanrı'da huzur bul, Çünkü umudum O'ndadır.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Tek kayam, kurtuluşum, Kalem O'dur, sarsılmam.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
Kurtuluşum ve onurum Tanrı'ya bağlıdır, Güçlü kayam, sığınağım O'dur.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Ey halkım, her zaman O'na güven, İçini dök O'na, Çünkü Tanrı sığınağımızdır. (Sela)
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Sıradan insan ancak bir soluk, Soylu insansa bir yalandır. Tartıya konduğunda ikisi birlikte soluktan hafiftir.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Zorbalığa güvenmeyin, yağma malla övünmeyin; Varlığınız artsa bile, ona gönül bağlamayın.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
Tanrı bir şey söyledi, Ben iki şey duydum: Güç Tanrı'nındır,
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
Sevgi de senin, ya Rab! Çünkü sen herkese, yaptığının karşılığını verirsin.

< Zabura 62 >