< Zabura 62 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
Ta, u Boga je mir duši mojoj, od njega je spasenje moje!
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Ta, on je grad moj i spasenje moje, utoèište moje, neæu posrnuti nimalo.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
Dokle æete napadati na èovjeka? Svi hoæete da ga oborite kao zid navaljen, kao ogradu isprovaljivanu.
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
Baš naumiše da ga svrgnu s visine, omilje im laž, ustima blagosiljaju a u srcu kunu.
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
Da, u Bogu se smiri, dušo moja; jer je u njemu nad moj.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
On je grad moj i spasenje moje, utoèište moje, neæu posrnuti.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
U Bogu je spasenje moje i slava moja, tvrdi grad i pristanište meni je u Bogu.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Narode! uzdaj se u njega u svako doba; izlivajte pred njim srce svoje; Bog je naše utoèište.
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Ta, sinovi su prostaèki ništa, sinovi su gospodski laž, da se metnu na mjerila, bili bi lakši nego ništa.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Ne uzdajte se u vlast ni u otimanje, nemojte biti ništavi; kad raste bogatstvo, ne dajte da vam srce prione za nj.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
Jednom reèe Bog i više puta èuh, da je krjepost u Boga.
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
I u tebe je, Gospode, milost; jer ti plaæaš svakome po djelima njegovijem.