< Zabura 62 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
برای یدوتون سالار مغنیان. مزمور داود جان من فقط برای خدا خاموش می شود زیرا که نجات من از جانب اوست.۱
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
او تنها صخره و نجات من است و قلعه بلند من. پس بسیار جنبش نخواهم خورد.۲
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
تا به کی بر مردی هجوم می‌آورید تا همگی شما او راهلاک کنید مثل دیوار خمشده و حصار جنبش خورده؟۳
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
در این فقط مشورت می‌کنند که او را ازمرتبه‌اش بیندازند. و دروغ را دوست می‌دارند. به زبان خود برکت می‌دهند و در دل خود لعنت می‌کنند، سلاه.۴
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
‌ای جان من فقط برای خدا خاموش شو زیراکه امید من از وی است.۵
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
او تنها صخره و نجات من است و قلعه بلند من تا جنبش نخورم.۶
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
برخداست نجات و جلال من. صخره قوت من وپناه من در خداست.۷
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
‌ای قوم همه وقت بر اوتوکل کنید و دلهای خود را به حضور وی بریزید. زیرا خدا ملجای ماست، سلاه.۸
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
البته بنی آدم بطالت‌اند و بنی بشر دروغ. در ترازو بالا می‌روندزیرا جمیع از بطالت سبکترند.۹
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
بر ظلم توکل مکنید و بر غارت مغرور مشوید. چون دولت افزوده شود دل در آن مبندید.۱۰
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
خدا یک بارگفته است و دو بار این را شنیده‌ام که قوت از آن خداست.۱۱
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
‌ای خداوند رحمت نیز از آن تواست، زیرا به هر کس موافق عملش جزا خواهی داد.۱۲

< Zabura 62 >