< Zabura 62 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
Pour le chef musicien. A Jeduthun. Un psaume de David. Mon âme repose en Dieu seul. Mon salut vient de lui.
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Lui seul est mon rocher, mon salut et ma forteresse. Je ne serai jamais fortement ébranlé.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
Combien de temps allez-vous agresser un homme? Vous voulez tous le jeter à terre, comme un mur penché, comme une clôture chancelante?
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
Ils ont bien l'intention de le jeter à bas de sa position élevée. Ils se délectent de mensonges. Ils bénissent de la bouche, mais ils maudissent intérieurement. (Selah)
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
Mon âme, attends en silence Dieu seul, car c'est de lui que je m'attends.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Lui seul est mon rocher, mon salut, ma forteresse. Je ne serai pas ébranlé.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
Mon salut et mon honneur sont auprès de Dieu. Le rocher de ma force, et mon refuge, est en Dieu.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Ayez confiance en lui en tout temps, vous autres. Répandez votre cœur devant lui. Dieu est un refuge pour nous. (Selah)
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Les hommes de peu de valeur ne sont qu'un souffle, et les hommes de haut rang sont un mensonge. Dans les soldes, ils vont augmenter. Ils sont ensemble plus légers qu'un souffle.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Ne vous fiez pas à l'oppression. Ne devenez pas vaniteux dans le vol. Si les richesses augmentent, n'y attachez pas votre cœur.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
Dieu a parlé une fois; J'ai entendu cela deux fois, ce pouvoir appartient à Dieu.
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
A toi aussi, Seigneur, appartient la bonté, car tu récompenses chaque homme selon son travail.