< Zabura 62 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
For the chief musician; after the manner of Jeduthun. A psalm of David. I wait in silence for God alone; my salvation comes from him.
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
He alone is my rock and my salvation; he is my high tower; I will not be greatly moved.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
How long, all of you, will you attack a man, that you may tip him over like a leaning wall or a shaky fence?
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
They consult with him only to bring him down from his honorable position; they love to tell lies; they bless him with their mouths, but in their hearts they curse him. (Selah)
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
I wait in silence for God alone; for my hope is set on him.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
He alone is my rock and my salvation; he is my high tower; I will not be moved.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
With God is my salvation and my glory; the rock of my strength and my refuge are in God.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Trust in him at all times, you people; pour out your heart before him; God is a refuge for us. (Selah)
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Surely men of low standing are vanity, and men of high standing are a lie; they will weigh lightly in the scales; weighed together, they are lighter than nothing.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Do not trust in oppression or robbery; and do not hope uselessly in riches, for they will bear no fruit; do not fix your heart on them.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
God has spoken once, twice have I heard this: power belongs to God.
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
Also to you, Lord, belongs covenant faithfulness, for you pay back every person for what he has done.