< Zabura 62 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
To the choirmaster on Jeduthun a psalm of David. Only [is] with God silence being my [is] from him salvation my.
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Only he [is] rock my and salvation my refuge my not I will be shaken much.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
Until when? - will you attack on a person you will be murdered all of you like a wall bent down a fence pushed down.
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
Surely from loftiness his - they have planned to thrust [him] down they are pleased with falsehood with mouth his they bless and in inner being their they curse (Selah)
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
Only to God be silent O self my for that [is] from him hope my.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Only he [is] rock my and salvation my refuge my not I will be shaken.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
[is] on God salvation my and honor my [the] rock of strength my refuge my [is] in God.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Trust in him at every time - O people pour out before him heart your God [is] a refuge of us (Selah)
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Only - [are] a breath [the] children of humankind [are] falsehood [the] children of everyone in [the] balances to go up they [are] more than a breath together.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
May not you trust in extortion and in robbery may not you put vain hope wealth - if it will bear fruit may not you set heart.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
One [time] - he has spoken God two [times] this I have heard that strength [belongs] to God.
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
And [belongs] to you O Lord covenant loyalty for you you repay to a person according to work his.

< Zabura 62 >