< Zabura 62 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
“For the leader of the music of the Jeduthunites, A psalm of David.” Truly my soul resteth on God alone; From him cometh my deliverance!
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
He alone is my rock and my salvation; He is my safeguard, I shall not wholly fall!
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
How long will ye continue to assault a single man? How long will ye all seek to destroy me, Like a bending wall, or a tottering fence?
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
They study how to cast me down from my eminence; They delight in falsehood; They bless with their mouths, but in their hearts they curse.
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
My soul, rest thou on God alone, For from him cometh my hope!
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
He alone is my rock and my salvation; He is my safeguard, —I shall not fall.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
From God cometh my help and my glory: My strong rock, my refuge, is God.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Trust in him at all times, ye people! Pour out your hearts before him! God is our refuge!
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Truly men of low degree are vanity, And men of high degree are a lie; Placed in the balance, They are all lighter than vanity.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Trust not in extortion; Place no vain hopes in rapine! If riches increase, set not your heart upon them!
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
Once hath God promised, twice have I heard it, That power belongeth unto God.
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
To thee also, O Lord! belongeth mercy; For thou dost render to every man according to his work!