< Zabura 62 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
To the excelletn musician Ieduthun. A Psalme of David. Yet my soule keepeth silence vnto God: of him commeth my saluation.
2 Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Yet he is my strength and my saluation, and my defence: therefore I shall not much be mooued.
3 Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
How long wil ye imagine mischiefe against a man? ye shalbe all slaine: ye shalbe as a bowed wall, or as a wall shaken.
4 Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
Yet they consult to cast him downe from his dignitie: their delight is in lies, they blesse with their mouthes, but curse with their hearts. (Selah)
5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
Yet my soule keepe thou silence vnto God: for mine hope is in him.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
Yet is hee my strength, and my saluation, and my defence: therefore I shall not be mooued.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
In God is my saluation and my glory, the rocke of my strength: in God is my trust.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
Trust in him alway, ye people: powre out your hearts before him, for God is our hope. (Selah)
9 Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
Yet the children of men are vanitie, the chiefe men are lies: to lay them vpon a balance they are altogether lighter then vanitie.
10 Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
Trust not in oppression nor in robberie: be not vaine: if riches increase, set not your heart thereon.
11 Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
God spake once or twise, I haue heard it, that power belongeth vnto God,
12 kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”
And to thee, O Lord, mercie: for thou rewardest euery one according to his worke.

< Zabura 62 >