< Zabura 61 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
Oye, o! Dios, mi clamor; está atento a mi oración.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
Desde el cabo de la tierra clamaré a ti, cuando desmayare mi corazón; a la peña más alta que yo, llévame.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
Porque tú has sido mi refugio; torre de fortaleza delante del enemigo.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
Yo habitaré en tu tabernáculo para siempre; estaré seguro en el escondedero de tus alas.
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
Porque tú, o! Dios, has oído mis votos; has dado heredad a los que temen tu nombre.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Días sobre días añadirás al rey: sus años serán como generación y generación.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
El estará para siempre delante de Dios; misericordia y verdad apercibe que le conserven.
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
Así cantaré tu nombre para siempre, pagando mis votos cada día.

< Zabura 61 >