< Zabura 61 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
Til sangmesteren, på strengelek; av David. Hør, Gud, mitt klagerop, merk på min bønn!
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
Fra jordens ende roper jeg til dig, mens mitt hjerte vansmekter; før mig på en klippe, som ellers blir mig for høi!
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
For du har vært min tilflukt, et sterkt tårn imot fienden.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
La mig bo i ditt telt i all evighet, la mig finne ly i dine vingers skjul! (Sela)
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For du, Gud, har hørt på mine løfter, du har gitt mig arv med dem som frykter ditt navn.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Du vil legge dager til kongens dager, hans år skal være som slekt efter slekt,
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
han skal trone evindelig for Guds åsyn; sett miskunnhet og trofasthet til å bevare ham!
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
Så vil jeg lovsynge ditt navn til evig tid, forat jeg kan innfri mine løfter dag efter dag.

< Zabura 61 >