< Zabura 61 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
in finem in hymnis David exaudi Deus deprecationem meam intende orationi meae
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
a finibus terrae ad te clamavi dum anxiaretur cor meum in petra exaltasti me deduxisti me
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
quia factus es spes mea turris fortitudinis a facie inimici
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
inhabitabo in tabernaculo tuo in saecula protegar in velamento alarum tuarum diapsalma
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
quoniam tu Deus meus exaudisti orationem meam dedisti hereditatem timentibus nomen tuum
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
dies super dies regis adicies annos eius usque in diem generationis et generationis
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
permanet in aeternum in conspectu Dei misericordiam et veritatem quis requiret eius
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
sic psalmum dicam nomini tuo in saeculum saeculi ut reddam vota mea de die in diem