< Zabura 61 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
Pour le chef musicien. Pour un instrument à cordes. Par David. Entends mon cri, Dieu. Écoutez ma prière.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
De l'extrémité de la terre, je t'appellerai quand mon cœur sera accablé. Conduis-moi au rocher qui est plus haut que moi.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
Car tu as été pour moi un refuge, une tour forte de l'ennemi.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
J'habiterai dans ta tente pour toujours. Je me réfugierai sous l'abri de tes ailes. (Selah)
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
Car toi, Dieu, tu as entendu mes vœux. Tu m'as donné l'héritage de ceux qui craignent ton nom.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Tu prolongeras la vie du roi. Ses années seront pour des générations.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
Il sera intronisé dans la présence de Dieu pour toujours. Nommez votre bonté et votre vérité, afin qu'elles le préservent.
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
Et je chanterai à jamais les louanges de ton nom, pour que je puisse accomplir mes vœux quotidiennement.