< Zabura 61 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
To the victorie on orgun, to Dauid hym silf. God, here thou my biseching; yyue thou tent to my preyer.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
Fro the endis of the lond Y criede to thee; the while myn herte was angwischid, thou enhaunsidist me in a stoon.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
Thou laddest me forth, for thou art maad myn hope; a tour of strengthe fro the face of the enemye.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
I schal dwelle in thi tabernacle in to worldis; Y schal be keuered in the hilyng of thi wengis.
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For thou, my God, hast herd my preier; thou hast youe eritage to hem that dreden thi name.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Thou schalt adde daies on the daies of the king; hise yeeris til in to the dai of generacioun and of generacioun.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
He dwellith with outen ende in the siyt of God; who schal seke the merci and treuthe of hym?
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
So Y schal seie salm to thi name in to the world of world; that Y yelde my vowis fro dai in to dai.