< Zabura 61 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
Unto the end, in hymns, for David. Hear, O God, my supplication: be attentive to my prayer,
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
To thee have I cried from the ends of the earth: when my heart was in anguish, thou hast exalted me on a rock. Thou hast conducted me;
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
For thou hast been my hope; a tower of strength against the face of the enemy.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
In thy tabernacle I shall dwell for ever: I shall be protected under the covert of thy wings.
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For thou, my God, hast heard my prayer: thou hast given an inheritance to them that fear thy name.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Thou wilt add days to the days of the king: his years even to generation and generation.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
He abideth for ever in the sight of God: his mercy and truth who shall search?
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
So will I sing a psalm to thy name for ever and ever: that I may pay my vows from day to day.

< Zabura 61 >