< Zabura 61 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
To the chief Musician. On a stringed instrument. [A Psalm] of David. Hear, O God, my cry; attend unto my prayer.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
From the end of the earth will I call unto thee, when my heart is overwhelmed: thou wilt lead me on to a rock which is too high for me.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
For thou hast been a refuge for me, a strong tower from before the enemy.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
I will sojourn in thy tent for ever; I will take refuge in the covert of thy wings. (Selah)
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For thou, O God, hast heard my vows; thou hast given [me] the inheritance of those that fear thy name.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Thou wilt add days to the days of the king: his years shall be as many generations.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
He shall abide before God for ever: bestow loving-kindness and truth, that they may preserve him.
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
So will I sing forth thy name for ever, performing my vows from day to day.

< Zabura 61 >