< Zabura 61 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
Hear my cry, O God. Attend to my prayer.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
From the end of the earth I will call to thee when my heart is overwhelmed. Lead me to the rock that is higher than I.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
For thou have been a refuge for me, a strong tower from the enemy.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
I will dwell in thy tabernacle forever. I will take refuge in the covert of thy wings. (Selah)
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For thou, O God, have heard my vows. Thou have given me the heritage of those who fear thy name.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Thou will prolong the king's life. His years shall be as many generations.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
He shall abide before God forever. O prepare loving kindness and truth that they may preserve him.
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
So I will sing praise to thy name forever, that I may daily perform my vows.

< Zabura 61 >