< Zabura 60 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
Para el músico principal. Con la melodía de “El Lirio de la Alianza”. Un poema didáctico de David, cuando luchó con Aram Naharaim y con Aram Zobah, y Joab volvió, y mató a doce mil de Edom en el Valle de la Sal. Dios, nos has rechazado. Nos has destrozado. Te has enfadado. Restablézcanos, de nuevo.
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
Has hecho temblar la tierra. Lo has roto. Arreglar sus fracturas, porque tiembla.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
Has mostrado a tu pueblo cosas difíciles. Nos has hecho beber el vino que nos hace tambalear.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
Has dado un estandarte a los que te temen, para que se muestre por la verdad. (Selah)
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Para que tu amado sea liberado, salva con tu mano derecha, y respóndenos.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dios ha hablado desde su santuario: “Voy a triunfar. Dividiré Siquem, y medir el valle de Succoth.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Mío es Galaad y mío es Manasés. Efraín también es la defensa de mi cabeza. Judá es mi cetro.
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab es mi lavabo. Lanzaré mi sandalia sobre Edom. Grito de triunfo sobre Filistea”.
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
¿Quién me llevará a la ciudad fuerte? ¿Quién me ha llevado a Edom?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
¿No nos has rechazado, Dios, a nosotros? No sales con nuestros ejércitos, Dios.
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Danos ayuda contra el adversario, porque la ayuda del hombre es vana.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Por medio de Dios lo haremos con valentía, ya que es él quien va a pisotear a nuestros adversarios.

< Zabura 60 >