< Zabura 60 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
Para o músico chefe. Ao som de “O Lírio do Convênio”. Um poema didático de David, quando ele lutou com Aram Naharaim e com Aram Zobah, e Joab voltou, e matou doze mil Edom no Vale do Sal. God, você nos rejeitou. Você nos derrubou. Você tem ficado bravo. Restaure-nos, novamente.
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
Você fez a terra tremer. Você o rasgou. Consertar suas fraturas, por causa de seus tremores.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
Você tem mostrado ao seu povo coisas difíceis. Você nos fez beber o vinho que nos faz cambalear.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
Você deu um banner para aqueles que o temem, que pode ser exibido por causa da verdade. (Selah)
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
para que sua amada possa ser entregue, economize com sua mão direita e nos responda.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Deus falou a partir de seu santuário: “Eu vou triunfar. Vou dividir o Shechem, e medir o vale de Succoth.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Gilead é meu, e Manasseh é meu. Ephraim também é a defesa da minha cabeça. Judah é meu ceptro.
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab é o meu lavatório. Vou jogar minha sandália na Edom. Eu grito em triunfo sobre a Filístia”.
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
Quem me trará para a cidade forte? Quem me levou à Edom?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Haven você, Deus, não nos rejeitou? Você não sai com nossos exércitos, Deus.
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give nós ajudamos contra o adversário, pois a ajuda do homem é vaidosa.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Através de Deus, faremos valentemente, pois é ele quem vai pisar em nossos adversários.

< Zabura 60 >