< Zabura 60 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
Salmo “Mictão” de Davi, de ensinamento, para o regente, conforme “Susanedute”, quando lutou contra os de Arã-Naraim e Arã-Zobá, e Joabe voltou vitorioso, tendo ferido no Vale do Sal a doze mil dos de Edom: Deus, tu nos rejeitaste, e nos quebraste; tu te encheste de ira. [Por favor], restaura-nos!
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
Tu fizeste a terra tremer, [e] a abriste; cura suas rachaduras, porque ela está abalada.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
Mostraste ao teu povo coisas duras; nos fizeste beber vinho perturbador.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
Deste uma bandeira aos que te temem, para se refugiarem dos tiros de arco. (Selá)
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Para que os teus amados sejam livrados; salva-nos com tua mão direita, e responde-nos.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Deus falou em seu santuário: Eu me alegrarei; repartirei a Siquém e medirei o vale de Sucote.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Meu [é] Gileade, e meu [é] Manassés; e Efraim [é] a força de minha cabeça; Judá [é] meu legislador.
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moabe [é] minha bacia de lavar; sobre Edom lançarei minha sandália; gritarei de alegria sobre a Filístia.
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
Quem me levará a uma cidade fortificada? Quem me guiará até Edom?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Não serás tu, ó Deus, que tinha nos rejeitado? Não saías tu, ó Deus, com nossos exércitos?
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Dá-nos socorro para a angústia; porque a salvação de [origem] humana é inútil.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Com Deus faremos coisas grandiosas; e ele atropelará nossos adversários.