< Zabura 60 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
in finem his qui inmutabuntur in tituli inscriptione David in doctrina cum succendit Syriam Mesopotamiam et Syriam Soba et convertit Ioab et percussit vallem Salinarum duodecim milia Deus reppulisti nos et destruxisti nos iratus es et misertus es nobis
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
commovisti terram et turbasti eam sana contritiones eius quia commota est
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
ostendisti populo tuo dura potasti nos vino conpunctionis
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
dedisti metuentibus te significationem ut fugiant a facie arcus diapsalma ut liberentur dilecti tui
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
salvum fac dextera tua et exaudi me
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Deus locutus est in sancto suo laetabor et partibor Sicima et convallem tabernaculorum metibor
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
meus est Galaad et meus est Manasses et Effraim fortitudo capitis mei Iuda rex meus
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab olla spei meae in Idumeam extendam calciamentum meum mihi alienigenae subditi sunt
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
quis deducet me in civitatem munitam quis deducet me usque in Idumeam
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
nonne tu Deus qui reppulisti nos et non egredieris Deus in virtutibus nostris
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
da nobis auxilium de tribulatione et vana salus hominis
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
in Deo faciemus virtutem et ipse ad nihilum deducet tribulantes nos