< Zabura 60 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
In finem, pro his qui immutabuntur, in tituli inscriptionem ipsi David, in doctrinam, cum succendit Mesopotamiam Syriæ et Sobal, et convertit Joab, et percussit Idumæam in valle Salinarum duodecim millia. [Deus, repulisti nos, et destruxisti nos; iratus es, et misertus es nobis.
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
Commovisti terram, et conturbasti eam; sana contritiones ejus, quia commota est.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
Ostendisti populo tuo dura; potasti nos vino compunctionis.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
Dedisti metuentibus te significationem, ut fugiant a facie arcus; ut liberentur dilecti tui.
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Salvum fac dextera tua, et exaudi me.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Deus locutus est in sancto suo: lætabor, et partibor Sichimam; et convallem tabernaculorum metibor.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Meus est Galaad, et meus est Manasses; et Ephraim fortitudo capitis mei. Juda rex meus;
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab olla spei meæ. In Idumæam extendam calceamentum meum: mihi alienigenæ subditi sunt.
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
Quis deducet me in civitatem munitam? quis deducet me usque in Idumæam?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
nonne tu, Deus, qui repulisti nos? et non egredieris, Deus, in virtutibus nostris?
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Da nobis auxilium de tribulatione, quia vana salus hominis.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
In Deo faciemus virtutem; et ipse ad nihilum deducet tribulantes nos.]

< Zabura 60 >