< Zabura 60 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
[I prayed], “God, you have rejected us [Israelis]! Because you have been angry [with us], you have [enabled our enemies] to break through our ranks. [Please] enable us to be strong again!
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
[When we were defeated, it was as though] [MET] there was a big earthquake in our land that caused the ground to split open. So now, [just as only you can] cause the cracks in the land to disappear, [help our army to be strong again], because [it is as though] our country is (falling apart/being destroyed).
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
You have caused [us], your people, to suffer very much; [it is as though] you forced us to drink [strong] wine that caused us to stagger around [after we became drunk].
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
But you have raised a battle flag for those who revere you in order that they can gather around it and not [be killed by the enemies’] arrows.
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Answer our [prayers] and enable us by your power [MTY] to defeat [our enemies] in order that we, the people whom you love, will be saved.”
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
[Then] God [answered my prayer and] spoke from his temple, saying, “Because I have conquered [your enemies], I will divide up [everything in] Shechem [city], and I will distribute it among my people [the land in] Succoth Valley.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
The Gilead [region] is mine; the [people of the tribe of] Manasseh are mine; [the tribe of] Ephraim is [like] my helmet [MET]; and [the tribe of] Judah is [like] the (scepter/stick [that I hold which shows that I am the ruler]) [MET];
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
but the Moab [region] is [like] my washbasin [MET]; I throw my sandal in the Edom [area to show that it belongs to me]; I shout triumphantly because I have defeated [the people of] the Philistia [area].”
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
[Because I want to defeat the people of] Edom, (who will lead my [army triumphantly] to their [capital] city that has strong walls around it?/I want someone to lead my [army triumphantly] to their [capital] city that has strong walls around it.)” [RHQ]
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
So, God, we [desire/hope that] [RHQ] you have not truly abandoned us, and that you will go with us when our armies march out [to fight our enemies].
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
[We need you to] help us when we fight against our enemies, because the help that humans can give us is worthless.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
But with you [helping us], we shall win; you will enable us to defeat our enemies.

< Zabura 60 >