< Zabura 60 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
To him that excelleth upon Shushan Eduth, or Michtam. A Psalme of David to teach. When he fought against Aram Naharaim, and against Aram Zobah, when Joab returned and slew twelve thousand Edomites in the salt valley. O God, thou hast cast vs out, thou hast scattered vs, thou hast bene angry, turne againe vnto vs.
2 Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
Thou hast made the land to tremble, and hast made it to gape: heale the breaches thereof, for it is shaken.
3 Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
Thou hast shewed thy people heauy things: thou hast made vs to drinke the wine of giddines.
4 Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
But now thou hast giuen a banner to them that feare thee, that it may be displayed because of thy trueth. (Selah)
5 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
That thy beloued may be deliuered, helpe with thy right hand and heare me.
6 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God hath spoken in his holines: therefore I will reioyce: I shall deuide Shechem, and measure the valley of Succoth.
7 Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
Gilead shalbe mine, and Manasseh shalbe mine: Ephraim also shalbe the strength of mine head: Iudah is my lawgiuer.
8 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
Moab shalbe my wash pot: ouer Edom will I cast out my shoe: Palestina shew thy selfe ioyfull for me.
9 Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
Who will leade me into the strong citie? who will bring me vnto Edom?
10 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Wilt not thou, O God, which hadest cast vs off, and didest not go forth, O God, with our armies?
11 Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Giue vs helpe against trouble: for vaine is the helpe of man.
12 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Through God we shall doe valiantly: for he shall tread downe our enemies.