< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Müzik şefi için - Sekiz telli sazlarla Davut'un mezmuru Ya RAB, öfkeyle azarlama beni, Gazapla yola getirme.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Lütfet bana, ya RAB, bitkinim; Şifa ver bana, ya RAB, kemiklerim sızlıyor,
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Çok acı çekiyorum. Ah, ya RAB! Ne zamana dek sürecek bu?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Gel, ya RAB, kurtar beni, Yardım et sevginden dolayı.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
Çünkü ölüler arasında kimse seni anmaz, Kim şükür sunar sana ölüler diyarından? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
İnleye inleye bittim, Döşeğim su içinde bütün gece ağlamaktan, Yatağım sırılsıklam gözyaşlarımdan.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Kederden gözlerimin feri sönüyor, Zayıflıyor gözlerim düşmanlarım yüzünden.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Ey kötülük yapanlar, Uzak durun benden, Çünkü RAB ağlayışımı işitti.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
Yalvarışımı duydu, Duamı kabul etti.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Bütün düşmanlarım utanacak, Hepsini dehşet saracak, Ansızın geri dönecekler utanç içinde.

< Zabura 6 >