< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Para el músico principal; en instrumentos de cuerda, en la lira de ocho cuerdas. Un salmo de David. Yahvé, no me reprendas en tu ira, ni me disciplinas en tu ira.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Ten piedad de mí, Yahvé, porque estoy desfallecido. Yahvé, sáname, porque mis huesos están turbados.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Mi alma también está muy angustiada. Pero tú, Yahvé, ¿hasta cuándo?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Vuelve, Yahvé. Libera mi alma, y sálvame por tu amorosa bondad.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
Porque en la muerte no hay memoria de ti. En el Seol, ¿quién te dará las gracias? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
Estoy cansado de mis gemidos. Cada noche inundo mi cama. Empapo mi sofá con mis lágrimas.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Mi ojo se consume por la pena. Envejece por culpa de todos mis adversarios.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Apartaos de mí, todos los obreros de la iniquidad, porque Yahvé ha escuchado la voz de mi llanto.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
Yahvé ha escuchado mi súplica. Yahvé acepta mi oración.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Que todos mis enemigos se avergüencen y queden consternados. Se volverán atrás, serán deshonrados de repente.

< Zabura 6 >