< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Senhor, não me reprehendas na tua ira, nem me castigues no teu furor.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Tem misericordia de mim, Senhor, porque sou fraco: sara-me, Senhor, porque os meus ossos estão perturbados.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Até a minha alma está perturbada; mas tu, Senhor, até quando?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Volta-te, Senhor, livra a minha alma: salva-me por tua benignidade.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
Porque na morte não ha lembrança de ti; no sepulchro quem te louvará? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
Já estou cançado do meu gemido, toda a noite faço nadar a minha cama; molho o meu leito com as minhas lagrimas.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Já os meus olhos estão consumidos pela magoa, e teem-se envelhecido por causa de todos os meus inimigos.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Apartae-vos de mim todos os que obraes a iniquidade; porque o Senhor já ouviu a voz do meu pranto.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
O Senhor já ouviu a minha supplica; o Senhor acceitará a minha oração.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Envergonhem-se e perturbem-se todos os meus inimigos; tornem atraz e envergonhem-se n'um momento.

< Zabura 6 >