< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
다윗의 시, 영장으로 현악 스미닛에 맞춘 노래 여호와여 주의 분으로 나를 견책하지 마옵시며 주의 진노로 나를 징계하지 마옵소서
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
여호와여 내가 수척하였사오니 긍휼히 여기소서 여호와여 나의 뼈가 떨리오니 나를 고치소서
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
나의 영혼도 심히 떨리나이다 여호와여 어느 때까지니이까
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
여호와여 돌아와 나의 영혼을 건지시며 주의 인자하심을 인하여 나을 구원하소서
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
사망 중에서는 주를 기억함이 없사오니 음부에서 주께 감사할 자 누구리이까 (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
내가 탄식함으로 곤핍하여 밤마다 눈물로 내 침상을 띄우며 내 요를 적시나이다
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
내 눈이 근심을 인하여 쇠하며 내 모든 대적을 인하여 어두웠나이다
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
행악하는 너희는 다 나를 떠나라 여호와께서 내 곡성을 들으셨도다
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
여호와께서 내 간구를 들으셨음이여 여호와께서 내 기도를 받으시리로다
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
내 모든 원수가 부끄러움을 당하고 심히 떪이여 홀연히 부끄러워 물러가리로다

< Zabura 6 >