< Zabura 6 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Dem Sangmeister, auf der Oktave mit Saitenspiel. Ein Psalm Davids. Jehovah, strafe mich nicht in Deinem Zorn, und züchtige mich nicht in Deinem Grimm.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Sei gnädig mir, Jehovah; denn ich verschmachte. Heile mich, Jehovah; denn meine Gebeine sind bestürzt.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Und meine Seele ist sehr bestürzt. Und Du, Jehovah, wie lange.
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Kehre zurück, Jehovah, befreie meine Seele, rette mich um Deiner Barmherzigkeit willen!
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
Denn man gedenkt Dein nicht im Tode. Wer in der Hölle bekennt Dich? (Sheol )
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
Ich bin müde von meinem Seufzen, schwemme die ganze Nacht mein Bett, netze mit meinen Tränen mein Ruhebett.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Mein Auge schmachtet vor Verdruß, ist alt geworden ob aller meiner Dränger.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Weicht ab von mir alle, die ihr Unrecht tut; denn Jehovah hört auf die Stimme meines Weinens.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
Jehovah hat gehört mein Flehen. Jehovah nimmt an mein Gebet.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Beschämt werden alle meine Feinde und sehr bestürzt; zurückkehren sie beschämt im Augenblick.