< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Au chef des chantres. Avec instruments à cordes. Sur la harpe à huit cordes. Psaume de David. Éternel! ne me punis pas dans ta colère, Et ne me châtie pas dans ta fureur.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Aie pitié de moi, Éternel! Car je suis sans force; Guéris-moi, Éternel! Car mes os sont tremblants.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
Mon âme est toute troublée; Et toi, Éternel! Jusques à quand?…
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Reviens, Éternel! Délivre mon âme; Sauve-moi, à cause de ta miséricorde.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
Car celui qui meurt n’a plus ton souvenir; Qui te louera dans le séjour des morts? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
Je m’épuise à force de gémir; Chaque nuit ma couche est baignée de mes larmes, Mon lit est arrosé de mes pleurs.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
J’ai le visage usé par le chagrin; Tous ceux qui me persécutent le font vieillir.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Éloignez-vous de moi, vous tous qui faites le mal! Car l’Éternel entend la voix de mes larmes;
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
L’Éternel exauce mes supplications, L’Éternel accueille ma prière.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
Tous mes ennemis sont confondus, saisis d’épouvante; Ils reculent, soudain couverts de honte.

< Zabura 6 >