< Zabura 6 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
For the Chief Musician; on stringed instruments, upon the eight-stringed lyre. A Psalm by David. Yahweh, don’t rebuke me in your anger, neither discipline me in your wrath.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Have mercy on me, Yahweh, for I am faint. Yahweh, heal me, for my bones are troubled.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
My soul is also in great anguish. But you, Yahweh—how long?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Return, Yahweh. Deliver my soul, and save me for your loving kindness’ sake.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
For in death there is no memory of you. In Sheol, who shall give you thanks? (Sheol )
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
I am weary with my groaning. Every night I flood my bed. I drench my couch with my tears.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
My eye wastes away because of grief. It grows old because of all my adversaries.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Depart from me, all you workers of iniquity, for Yahweh has heard the voice of my weeping.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
Yahweh has heard my supplication. Yahweh accepts my prayer.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
May all my enemies be ashamed and dismayed. They shall turn back, they shall be disgraced suddenly.