< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
“For the leader of the music; to be accompanied with stringed instruments; to the octave. A psalm of David.” O LORD! rebuke me not in thine anger; Chasten me not in thy hot displeasure!
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Have pity upon me, O LORD! for I am weak; Heal me, O LORD! for my bones tremble!
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
My soul, also, is sore troubled; And thou, O LORD! how long—?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Return, O LORD! and deliver me; Oh, save me according to thy mercy!
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
For in death no praise is given to thee; In the underworld who can give thee thanks? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
I am weary with my groaning; All the night I make my bed to swim, And drench my couch with my tears.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Mine eye is wasted with grief; It hath become old because of all my enemies.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Depart from me, all ye that do iniquity; For the LORD heareth the voice of my weeping.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
The LORD heareth my supplication; The LORD accepteth my prayer.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
All my enemies shall be ashamed and utterly confounded; They shall be turned back, and put to shame suddenly.

< Zabura 6 >