< Zabura 6 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
For the Leader; with string-music; on the Sheminith. A Psalm of David. O LORD, rebuke me not in Thine anger, neither chasten me in Thy wrath.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Be gracious unto me, O LORD, for I languish away; heal me, O LORD, for my bones are affrighted.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
My soul also is sore affrighted; and Thou, O LORD, how long?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Return, O LORD, deliver my soul; save me for Thy mercy's sake.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
For in death there is no remembrance of Thee; in the nether-world who will give Thee thanks? (Sheol )
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
I am weary with my groaning; every night make I my bed to swim; I melt away my couch with my tears.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
Mine eye is dimmed because of vexation; it waxeth old because of all mine adversaries.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Depart from me, all ye workers of iniquity; for the LORD hath heard the voice of my weeping.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
The LORD hath heard my supplication; the LORD receiveth my prayer.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
All mine enemies shall be ashamed and sore affrighted; they shall turn back, they shall be ashamed suddenly.