< Zabura 6 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
For the choirmaster. With stringed instruments, according to Sheminith. A Psalm of David. O LORD, do not rebuke me in Your anger or discipline me in Your wrath.
2 Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
Be merciful to me, O LORD, for I am frail; heal me, O LORD, for my bones are in agony.
3 Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
My soul is deeply distressed. How long, O LORD, how long?
4 Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
Turn, O LORD, and deliver my soul; save me because of Your loving devotion.
5 Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
For there is no mention of You in death; who can praise You from Sheol? (Sheol h7585)
6 Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
I am weary from groaning; all night I flood my bed with weeping and drench my couch with tears.
7 Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
My eyes fail from grief; they grow dim because of all my foes.
8 Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
Depart from me, all you workers of iniquity, for the LORD has heard my weeping.
9 Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
The LORD has heard my cry for mercy; the LORD accepts my prayer.
10 Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.
All my enemies will be ashamed and dismayed; they will turn back in sudden disgrace.

< Zabura 6 >