< Zabura 59 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
Načelniku godbe: "Ne pogubi"; Davidova pesem odlična; ko je bil poslal Savel može, ki so ogledavali hišo njegovo, da bi ga umorili. Reši me sovražnikov mojih, moj Bog; nad nje, ki se spenjajo v méne, povzdigni me.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Reši me njih, ki delajo krivico, in ljudî krvoločnih otmi me.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
Ker, glej, življenje moje zalezujejo, shajajo se zoper mene krepki, brez hudobije moje, brez greha mojega, Gospod!
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
Brez krivice moje se zbirajo in pripravljajo: vstani meni naproti in ozri se.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
Ti torej, Gospod, Bog vojnih krdél, Bog Izraelov, zbúdi se, obiskat vse one narode: ne bodi milosten nikomur, ki dela krivico, nezvesto.
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Povračajo se zvečer; bevkajo kakor pes, in obdajajo mesto.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Glej, bljujejo z usti svojimi, z mečem na ustnah svojih; ker kdo sliši? pravijo.
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
Ti pa, Gospod, bodeš se jim smijal, zasmehoval bodeš vse tiste narode.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
Ko ima on moč, gledal bodem v té, ker Bog je moj grad.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
Bog milosti moje bode me prestregel; Bog storí, da bodem gledal sovražnike svoje.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Ne pobij jih, da ne pozabijo rojaki moji; izženi jih s krepostjo svojo, in pahni jih dol, ščit naš, Gospod!
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
Greh njih ust je njih ustnic beseda; ko bodejo vjeti v napuhu svojem, tedaj naj oznanjajo od prekletstva, tedaj od slabosti.
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Pokončaj v srdu, pokončaj, da jih ne bode več; vedó naj, da Bog gospoduje v Jakobu do mej zemlje.
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Ko se povračajo zvečer, bevkajo naj kakor pes, in obdajajo mesto.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
Sami se naj gonijo, da bi jedli; ko ne bodejo nasíteni, tedaj primorani naj bodejo prenočevati.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
Jaz pa bodem prepeval moč tvojo, in pel bodem do vsakega jutra milost tvojo, da si ti mi bil grad moj in pribežališče, ko sem bil v stiski.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
O moč moja, tebi bodem prepeval, da je Bog grad moj, Bog milosti moje.