< Zabura 59 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
For the Chief Musician. To the tune of “Do Not Destroy.” A poem by David, when Saul sent, and they watched the house to kill him. Deliver me from my enemies, my God. Set me on high from those who rise up against me.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Deliver me from the workers of iniquity. Save me from the bloodthirsty men.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
For, behold, they lie in wait for my soul. The mighty gather themselves together against me, not for my disobedience, nor for my sin, LORD.
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
I have done no wrong, yet they are ready to attack me. Rise up, behold, and help me!
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
You, LORD God of Armies, the God of Israel, rouse yourself to punish the nations. Show no mercy to the wicked traitors. (Selah)
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They return at evening, howling like dogs, and prowl around the city.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Behold, they spew with their mouth. Swords are in their lips, “For”, they say, “who hears us?”
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
But you, LORD, laugh at them. You scoff at all the nations.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
Oh, my Strength, I watch for you, for God is my high tower.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
My God will go before me with his loving kindness. God will let me look at my enemies in triumph.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Don’t kill them, or my people may forget. Scatter them by your power, and bring them down, Lord our shield.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
For the sin of their mouth, and the words of their lips, let them be caught in their pride, for the curses and lies which they utter.
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Consume them in wrath. Consume them, and they will be no more. Let them know that God rules in Jacob, to the ends of the earth. (Selah)
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
At evening let them return. Let them howl like a dog, and go around the city.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
They shall wander up and down for food, and wait all night if they aren’t satisfied.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
But I will sing of your strength. Yes, I will sing aloud of your loving kindness in the morning. For you have been my high tower, a refuge in the day of my distress.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
To you, my strength, I will sing praises. For God is my high tower, the God of my mercy.

< Zabura 59 >