< Zabura 59 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
God, save me from my enemies! Protect me from those who want to attack me!
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Rescue me from men who want to do what is wicked, men who are murderers!
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
Look! They are waiting to kill me! Fierce men have gathered to assault me. Yahweh, they are doing that even though I have not done what is wrong!
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
It is not because I have committed any sin [against them] that they run and get ready to attack me.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
Yahweh my God, commander of the armies of heaven, the one we Israelis [worship], arise and punish the [ungodly/heathen people of] all the nations; do not be merciful to those [wicked people] who have (acted treacherously toward/secretly planned to harm) us.
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They return each evening, snarling like vicious dogs [SIM] as they prowl around this city.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
They loudly say terrible things; they say [MTY] many things that [injure people like] [MET] swords do, but they think, “No one will [RHQ] hear us!”
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
But Yahweh, you laugh at them. You (scoff at/ridicule) the [people of the pagan] nations.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
God, I have confidence in you because you are very strong; you are my refuge.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
Because you love me, you will come to save me; you will allow me to watch while you defeat my enemies.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
But do not kill them [immediately] in order that my people will not forget [how you punished them]! [Instead], Lord, [you who are like a] shield [that protects us] [MET], scatter them by your power, and [then] defeat them.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
Because what they say [MTY] is sinful, allow them to be trapped for being proud. Because they are [always] cursing and telling lies,
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
because you are angry, get rid of them; destroy them completely in order that people will know that you rule over us, your Israeli people, and that you rule over all the earth.
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
My enemies return each evening, snarling like [vicious] dogs as they prowl around this city.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
They roam around, searching for food; and if they do not find enough, they growl.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
But [as for me], I will sing about your power; [every] morning I will sing joyfully about your faithfully loving [us]. I will sing about how you protected me when I was [very] distressed.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
God, you are the one who enables me to be strong; you are my refuge; you faithfully love me.