< Zabura 59 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
Unto the end, destroy not, for David for an inscription of It title, when Saul sent and watched his house to kill him. Deliver me from my enemies, O my God; and defend me from them that rise up against me.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Deliver me from them that work iniquity, and save me from bloody men.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
For behold they have caught my soul: the mighty have rushed in upon me:
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
Neither is it my iniquity, nor my sin, O Lord: without iniquity have I run, and directed my steps.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
Rise up thou to meet me, and behold: even thou, O Lord, the God of hosts, the God of Israel. Attend to visit all the nations: have no mercy on all them that work iniquity.
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They shall return at evening, and shall suffer hunger like dogs: and shall go round about the city.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Behold they shall speak with their mouth, and a sword is in their lips: for who, say they, hath heard us?
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
But thou, O Lord, shalt laugh at them: thou shalt bring all the nations to nothing.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
I will keep my strength to thee: for thou art my protector:
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
My God, his mercy shall prevent me.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
God shall let me see over my enemies: slay them not, lest at any time my people forget. Scatter them by thy power; and bring them down, O Lord, my protector:
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
For the sin of their mouth, and the word of their lips: and let them be taken in their pride. And for their cursing and lying they shall be talked of,
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
When they are consumed: when they are consumed by thy wrath, and they shall be no more. And they shall know that God will rule Jacob, and all the ends of the earth.
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They shall return at evening and shall suffer hunger like dogs: and shall go round about the city.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
They shall be scattered abroad to eat, and shall murmur if they be not filled.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
But I will sing thy strength: and will extol thy mercy in the morning. For thou art become my support, and my refuge, in the day of my trouble.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
Unto thee, O my helper, will I sing, for thou art God my defence: my God my mercy.