< Zabura 59 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
For the choirmaster. To the tune of “Do Not Destroy.” A Miktam of David, when Saul sent men to watch David’s house in order to kill him. Deliver me from my enemies, O my God; protect me from those who rise against me.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Deliver me from workers of iniquity, and save me from men of bloodshed.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
See how they lie in wait for me. Fierce men conspire against me for no transgression or sin of my own, O LORD.
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
For no fault of my own, they move swiftly to attack me. Arise to help me, and take notice.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
O LORD God of Hosts, the God of Israel, rouse Yourself to punish all the nations; show no mercy to the wicked traitors.
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They return in the evening, snarling like dogs and prowling around the city.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
See what they spew from their mouths— sharp words from their lips: “For who can hear us?”
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
But You, O LORD, laugh at them; You scoff at all the nations.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
I will keep watch for You, O my strength, because You, O God, are my fortress.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
My God of loving devotion will come to meet me; God will let me stare down my foes.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Do not kill them, or my people will forget. Scatter them by Your power, and bring them down, O Lord, our shield.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
By the sins of their mouths and the words of their lips, let them be trapped in their pride, in the curses and lies they utter.
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Consume them in wrath; consume them till they are no more, so it may be known to the ends of the earth that God rules over Jacob.
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They return in the evening, snarling like dogs and prowling around the city.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
They scavenge for food, and growl if they are not satisfied.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
But I will sing of Your strength and proclaim Your loving devotion in the morning. For You are my fortress, my refuge in times of trouble.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
To You, O my strength, I sing praises, for You, O God, are my fortress, my God of loving devotion.