< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
¿Pronunciáis de verdad, o! congregación, justicia? ¿juzgáis rectamente hijos de Adam?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Antes de corazón obráis iniquidades en la tierra: violencia pesáis de vuestras manos.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
Extrañáronse los impíos desde la matriz: erraron desde el vientre hablando mentira.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Veneno tienen semejante al veneno de la serpiente: como áspide sordo que cierra su oreja.
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Que no oye la voz de los que encantan, del encantador sabio de encantamentos.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O! Dios, quiebra sus dientes en sus bocas: quiebra, o! Jehová, las muelas de los leoncillos.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Córranse como aguas que se van de suyo: armen sus saetas como si fuesen cortadas;
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Como el caracol que se deslie, vayan: como el abortivo de mujer, no vean el sol.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Antes que vuestras ollas sientan el fuego de las espinas; así vivos, así airado los arrebate con tempestad.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
Alegrarse ha el justo, cuando viere la venganza: sus pies lavará en la sangre del impío.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
Entonces dirá el hombre: Ciertamente hay fruto para el justo: ciertamente hay Dios que juzga en la tierra.

< Zabura 58 >