< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
Acaso fallaes vós devéras, ó congregação, a justiça? Julgaes realmente, ó filhos dos homens
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Antes no coração obraes perversidades: sobre a terra pesaes a violencia das vossas mãos.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
Alienam-se os impios desde a madre; andam errados desde que nasceram, fallando mentiras.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
O seu veneno é similhante ao veneno da serpente; são como a vibora surda que tapa os ouvidos,
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Para não ouvir a voz dos encantadores, do encantador sabio em encantamentos.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
Ó Deus, quebra-lhes os dentes nas suas boccas; arranca, Senhor, os dentes queixaes aos filhos dos leões.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Escorram como aguas que correm constantemente; quando elle armar as suas frechas, fiquem feitos em pedaços.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Como a lesma se derrete, assim se vá cada um d'elles, como o aborto d'uma mulher, que nunca viu o sol.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Antes que as vossas panellas sintam os espinhos, elle os arrebatará na sua indignação como com um redemoinho.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
O justo se alegrará quando vir a vingança; lavará os seus pés no sangue do impio.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
Então dirá o homem: Devéras ha uma recompensa para o justo; devéras ha um Deus que julga na terra.

< Zabura 58 >