< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
Est-ce que vous prononcez vraiment selon la justice? Fils des hommes, jugez-vous avec droiture?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Loin de là; dans votre cœur vous commettez des iniquités, vous ordonnez sur la terre la violence de vos mains.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
Les méchants se sont détournés dès le sein maternel; les menteurs se sont égarés dès leur naissance.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Ils ont un venin semblable au venin du serpent; ils sont comme l'aspic sourd, qui ferme son oreille;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Qui n'écoute point la voix des enchanteurs, la voix du charmeur expert en charmes.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O Dieu, brise-leur les dents dans la bouche! Éternel, romps les mâchoires des lionceaux!
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Qu'ils s'écoulent comme l'eau, et qu'ils se dissipent! Quand ils bandent leur arc, que leurs flèches soient rompues!
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Qu'ils s'en aillent comme le limaçon qui se fond; sans voir le soleil, comme l'avorton d'une femme!
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Avant que vos chaudières aient senti le feu des épines, vertes ou enflammées, le vent les emportera.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
Le juste se réjouira lorsqu'il aura vu la vengeance; il baignera ses pieds dans le sang du méchant.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
Et l'on dira: Oui, il y a du fruit pour le juste; oui, il y a un Dieu qui fait justice sur la terre.

< Zabura 58 >