< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
For the Chief Musician. To the tune of “Do Not Destroy.” A poem by David. Do you indeed speak righteousness, silent ones? Do you judge blamelessly, you sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
No, in your heart you plot injustice. You measure out the violence of your hands in the earth.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked go astray from the womb. They are wayward as soon as they are born, speaking lies.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their poison is like the poison of a snake, like a deaf cobra that stops its ear,
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
which doesn’t listen to the voice of charmers, no matter how skilful the charmer may be.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
Break their teeth, God, in their mouth. Break out the great teeth of the young lions, LORD.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Let them vanish like water that flows away. When they draw the bow, let their arrows be made blunt.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Let them be like a snail which melts and passes away, like the stillborn child, who has not seen the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots can feel the heat of the thorns, he will sweep away the green and the burning alike.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous shall rejoice when he sees the vengeance. He shall wash his feet in the blood of the wicked,
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
so that men shall say, “Most certainly there is a reward for the righteous. Most certainly there is a God who judges the earth.”

< Zabura 58 >