< Zabura 58 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
To the Chief Musician. "Do not Destroy." A precious Psalm, of David. Are ye, indeed, silent [when] righteousness, ye should speak? When, with equity, ye should judge, O ye sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Aye! ye all do work, perversity, —Throughout the land, your hands, weigh out, violence!
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
Lawless men have been estranged from birth, They have gone astray from their nativity, speaking falsehood;
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their poison, is like unto the poison of a serpent, Like the deaf adder, that stoppeth his ear;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
That will not hearken to the voice of whisperers, Though the wise one try to bind him with spells.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O God! break away their teeth in their mouth, The biters of the young lions, knock thou out, O Yahweh!
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Let such men flow away like waters that disperse themselves: He prepareth his arrow, Like [grass] let them be cut down:
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Like a snail, which melteth away as it goeth, An untimely birth of a woman, which hath not seen the sun:
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your kettles can perceive the [kindled] bramble, Be he green or be he withered, he shall be swept away.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous man will rejoice when he hath seen an avenging, His feet, will he bathe in the blood of the lawless one: —
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
So that a son of earth may say—Surely there is fruit for the righteous man! Surely there are gods who judge in the earth!