< Zabura 58 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
“For the leader of the music. To the tune of “Do not destroy.” A psalm of David.” Do ye, indeed, administer justice faithfully, ye mighty ones? Do ye judge with uprightness, ye sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Nay, in your hearts ye contrive iniquity; Your hands weigh out violence in the land!
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked are estranged, from their very birth; The liars go astray as soon as they are born.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
They have poison, like the poison of a serpent; Like the deaf adder's, which stoppeth her ear;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Which listeneth not to the voice of the charmer, And of the sorcerer, skilful in incantations.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
Break their teeth, O God! in their mouths! Break out the great teeth of the lions, O LORD!
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
May they melt like waters, which flow away; May their arrows, when they aim them, be as if cut in pieces!
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
May they be like the snail, which melteth away as it goeth; Like the abortion of a woman, that seeth not the sun!
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots feel the heat of the thorns, Whether fresh, or burning, may they be blown away!
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous shall rejoice, when he seeth such vengeance; He shall bathe his feet in the blood of the wicked.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
Then shall men say, “Truly there is a reward for the righteous! Truly there is a God who is judge upon the earth!”