< Zabura 58 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
TO THE OVERSEER. “DO NOT DESTROY.” A MIKTAM OF DAVID. Is it true, O silent one, that you speak righteously? Do you judge uprightly, O sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Even in heart you work iniquities, In the land you ponder the violence of your hands.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked have been estranged from the womb, They have erred from the belly, speaking lies.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their poison [is] as poison of a serpent, As a deaf cobra shutting its ear,
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Which does not listen to the voice of whisperers, A charmer of most skillful charms.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O God, break their teeth in their mouth, Break down the jaw-teeth of young lions, O YHWH.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
They are melted as waters, They go up and down for themselves, His arrow proceeds as they cut themselves off.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
He goes on as a snail that melts, [As] an untimely birth of a woman, They have not seen the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots discern the bramble, As living, He whirls away in His burning anger.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous rejoices that he has seen vengeance, He washes his steps in the blood of the wicked.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
And man says: “Surely fruit [is] for the righteous: Surely there is a God judging in the earth!”