< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
“To the chief musician Al-tashcheth, by David, a Michtham.” Do you indeed, who are dumb, speak righteously? do ye judge in uprightness, O ye sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Even in [your] heart ye work injustice: on the earth do ye weigh out the violence of your hands.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked are estranged [from goodness] from the womb: those who speak lies go astray from their very birth.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
They have poison like the poison of a serpent: [they are] like the deaf adder that stoppeth her ear;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Which will not hearken to the voice of conjurers, yea, that of the wisest of all charmers.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O God, break out their teeth in their mouth: the jaw-teeth of the young lions tear thou out, O Lord.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Let them melt away as water [which] runneth off: when each one bendeth [his bow to shoot] his arrows, let them be as if cut in pieces.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
As a snail which melteth, let him pass away; like the untimely birth of a woman which hath not seen the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots can feel the thorns, will he take them away with a whirlwind, both the green and the burning.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous will rejoice when he seeth the vengeance: he will bathe his steps in the blood of the wicked.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
So that a man shall say, Verily fruit will come for the righteous: verily there is a God that judgeth on the earth.

< Zabura 58 >