< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
For the end. Destroy not: by David, for a memorial. If you do indeed speak righteousness, [then] do you judge rightly, you sons of men.
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
For you work iniquities in [your] hearts in the earth: your hands plot unrighteousness.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
Sinners have gone astray from the womb: they go astray from the belly: they speak lies.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their venom is like [that] of a serpent; as [that] of a deaf asp, and that stops her ears;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
which will not hear the voice of charmers, nor [heed] the charm prepared skillfully by the wise.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
God has crushed their teeth in their mouth: God has broken the cheek-teeth of the lions.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
They shall utterly pass away like water running through: he shall bend his bow till they shall fail.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
They shall be destroyed as melted wax: the fire has fallen and they have not seen the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your thorns feel the white thorn, he shall swallow you up as living, as in his wrath.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous shall rejoice when he sees the vengeance of the ungodly: he shall wash his hands in the blood of the sinner.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
And a man shall say, Verily then there is a reward for the righteous: verily there is a God that judges them in the earth.

< Zabura 58 >