< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
For the choirmaster. To the tune of “Do Not Destroy.” A Miktam of David. Do you indeed speak justly, O rulers? Do you judge uprightly, O sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
No, in your hearts you devise injustice; with your hands you mete out violence on the earth.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked are estranged from the womb; the liars go astray from birth.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their venom is like the venom of a snake, like a cobra that shuts its ears,
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
refusing to hear the tune of the charmer who skillfully weaves his spell.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
O God, shatter their teeth in their mouths; O LORD, tear out the fangs of the lions.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
May they vanish like water that runs off; when they draw the bow, may their arrows be blunted.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
Like a slug that dissolves in its slime, like a woman’s stillborn child, may they never see the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots can feel the burning thorns— whether green or dry— He will sweep them away.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous will rejoice when they see they are avenged; they will wash their feet in the blood of the wicked.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
Then men will say, “There is surely a reward for the righteous! There is surely a God who judges the earth!”

< Zabura 58 >